8 Dukansu dakikai ne wawaye,Koyarwar gumaka ba wani abu bane, itace ne kawai!
9 An kawo fallayen azurfa dagaTarshish,Da zinariya kuma daga Ufaz,Aikin gwanaye da maƙeranzinariya.Tufafinsu na mulufi ne da shunayya,duka aikin gwanaye.
10 Amma Ubangiji shi ne Allah nagaskiya,Shi Allah mai rai ne,Shi Sarki ne madawwami.Saboda hasalarsa duniya ta girgiza,Al'ummai ba za su iya jurewa dafushinsa ba.
11 Haka za ku faɗa musu, “Gumakan da ba su yi sammai da duniya ba, za su lalace a duniya da a ƙarƙashin sammai.”
12 Shi ne, ta wurin ikonsa ya yi duniya,Ta wurin hikimarsa ya kafa ta,Ta wurin basirarsa kumaya ya shimfiɗasammai.
13 Sa'ad da ya yi murya akan ji ƙuginruwa a cikin sammaiYakan kawo ƙasashi daga ƙurewarduniya,Yakan yi walƙiyoyi saboda ruwansama,Daga cikin taskokinsa yakan kawoiska.
14 Kowane mutum dakiki ne, mararilimi,Kowane maƙerin zinariya zai shakunya saboda gumakansa,Gama siffofinsa ƙarya ne,Ba numfashi a cikinsu.