17 Zan mayar muku da lafiyarku,Zan kuma warkar da raunukanku,Ko da yake maƙiyanku sunakiranku yasassu,Suna cewa, ‘Ai, Sihiyona ce, bawanda ya kula da ita.’Ni Ubangiji na faɗa.”
18 Ubangiji ya ce,“Ga shi, zan komar wa alfarwarYakubu arzikinta,Zan kuma nuna wa wuraren zamansajinƙai,Za a sāke gina birnin a kufansa,Fādar kuma za ta kasance a indatake a dā.
19 Daga cikinsu za a ji waƙoƙin godiya.Da muryoyin masu murna.Zai riɓaɓɓanya su, ba za su zamakaɗan ba,Zan kuwa ɗaukaka su, ba za aƙasƙantar da su ba.
20 'Ya'yansu za su zama kamar dā,Jama'arsu kuma za su kahu agabana,Zan hukunta dukan waɗanda sukazalunce su.
21 Sarkinsu zai zama ɗaya dagacikinsu,Mai mulkinsu kuma zai fito dagacikinsu.Zan kawo shi kusa, zai kuwa kusaceni,Gama wane ne zai yi ƙarfin hali yakusace ni? Ni Ubangiji na faɗa.
22 Za ku zama mutanena,Ni kuwa zan zama Allahnku.”
23 Ga hadirin hasalar Ubangiji ya taso,wato iskar guguwa,Zai huce a kan mugaye.