6 Masu saurin gudu ba za su tsere ba,Haka nan kuma jarumi,A arewa a gefen Kogin Yufiretis,Sun yi tuntuɓe, sun fādi.
7 Wane ne wannan mai tashi kamarKogin Nilu,Kamar kogunan da ruwansu yakeambaliya?
8 Masar tana tashi kamar Nilu,Kamar kogunan da ruwansu yakeambaliya.Masar ta ce, “Zan tashi, in rufeduniya,Zan hallaka birane da mazaunacikinsu.”
9 Ku haura, ku dawakai,Ku yi sukuwar hauka, ku karusai!Bari sojoji su fito,Mutanen Habasha da Fut masuriƙon garkuwoyi,Da mutanen Lud, waɗanda suka iyariƙon baka.
10 Wannan rana ta Ubangiji, Allah MaiRunduna ce,Ranar ɗaukar fansa ce don ya ramawa maƙiyansa.Takobi zai ci, ya ƙoshi,Ya kuma sha jininsu, ya ƙoshi,Gama Ubangiji Allah Mai Rundunazai hallaka maƙiyansa,A arewa, a bakin Kogin Yufiretis.
11 Ku mutanen Masar, ku haura zuwaGileyadDon ku samo ganye!A banza kuke morar magunguna,Ba za ku warke ba.
12 Kunyarku ta kai cikin sauranal'umma,Kukanku kuma ya cika duniya.Soja na faɗuwa bisa kan soja.Dukansu biyu sun faɗi tare.