21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza, za a kuma ji muryar kukansu har a Bahar Maliya.
22 Wani zai tashi da sauri, ya yi sama kamar gaggafa. Zai buɗe fikafikansa a kan Bozara. Zukatan sojojin Edom za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.”
23 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Dimashƙu,“Hamat da Arfad sun gigice,Domin sun ji mugun labari,sun narke saboda yawan damuwa,Ba za su iya natsuwa ba.
24 Dimashƙu ta yi halin ƙaƙa naka yi,Ta juya, ta gudu,Tsoro ya kama ta,Azaba da baƙin ciki sun kama takamar na naƙuda.
25 Ƙaƙa aka manta da sanannen birni,Birnin da take cike da murna?
26 A waccan rana samarinta za su fāɗi adandalinta.Za a hallaka sojojinta duka,Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.
27 Zan kuma sa wuta a garun Dimashƙu,Za ta kuwa cinye fādodinBen-hadad.”