5 Allah na Isra'ila da Yahuza,Ubangiji Mai Runduna, bai yashesu ba,Ko da yake sun yi wa Mai Tsarki naIsra'ila zunubi.
6 Ku gudu daga cikin Babila,Bari kowa ya ceci ransa,Kada a hallaka ku tare da ita,Gama a wannan lokaci Ubangiji zaisāka mata,Zai sāka mata bisa ga alhakinta.
7 Babila ta zama ƙoƙon zinariya ahannun Ubangiji,Ta sa dukan duniya ta yi maye.Ƙasashen duniya sun sha ruwaninabinta, suka haukace.
8 Farat ɗaya, Babila ta fāɗi, takakkarye,Ku yi kuka dominta!Ku samo mata magani domin azabarda take sha, watakila ta warke.
9 Mun ba Babila magani, amma ba tawarke ba.Bari mu ƙyale ta, kowannenmu yakoma garinsu,Gama hukuncinta ya kai sammai, yayi tsawo har samaniya.
10 Ubangiji ya baratar da mu a fili,Bari mu tafi mu yi shelar aikinUbangiji Allahnmu a cikinSihiyona.
11 Ku wasa kibau, ku cikakwaruruwanku!Ubangiji ya ta da ruhun sarakunanMediyawa,Domin yana niyyar hallaka Babila.Gama Ubangiji zai yi ramuwasaboda Haikalinsa.