7 Babila ta zama ƙoƙon zinariya ahannun Ubangiji,Ta sa dukan duniya ta yi maye.Ƙasashen duniya sun sha ruwaninabinta, suka haukace.
8 Farat ɗaya, Babila ta fāɗi, takakkarye,Ku yi kuka dominta!Ku samo mata magani domin azabarda take sha, watakila ta warke.
9 Mun ba Babila magani, amma ba tawarke ba.Bari mu ƙyale ta, kowannenmu yakoma garinsu,Gama hukuncinta ya kai sammai, yayi tsawo har samaniya.
10 Ubangiji ya baratar da mu a fili,Bari mu tafi mu yi shelar aikinUbangiji Allahnmu a cikinSihiyona.
11 Ku wasa kibau, ku cikakwaruruwanku!Ubangiji ya ta da ruhun sarakunanMediyawa,Domin yana niyyar hallaka Babila.Gama Ubangiji zai yi ramuwasaboda Haikalinsa.
12 Ku ta da tuta don a faɗa wa garunBabila,Ku ƙarfafa matsara,Ku sa su su yi tsaro,Ku kuma sa 'yan kwanto!Ga shi, Ubangiji ya yi niyya, ya kuwaaikataAbin da ya faɗa a kan mazaunanBabila.
13 Ƙarshenki ya zo,Ke mai zama kusa da ruwa mai yawa,Mai yawan dukiya.Ajalinki ya auka.