8 Farat ɗaya, Babila ta fāɗi, takakkarye,Ku yi kuka dominta!Ku samo mata magani domin azabarda take sha, watakila ta warke.
9 Mun ba Babila magani, amma ba tawarke ba.Bari mu ƙyale ta, kowannenmu yakoma garinsu,Gama hukuncinta ya kai sammai, yayi tsawo har samaniya.
10 Ubangiji ya baratar da mu a fili,Bari mu tafi mu yi shelar aikinUbangiji Allahnmu a cikinSihiyona.
11 Ku wasa kibau, ku cikakwaruruwanku!Ubangiji ya ta da ruhun sarakunanMediyawa,Domin yana niyyar hallaka Babila.Gama Ubangiji zai yi ramuwasaboda Haikalinsa.
12 Ku ta da tuta don a faɗa wa garunBabila,Ku ƙarfafa matsara,Ku sa su su yi tsaro,Ku kuma sa 'yan kwanto!Ga shi, Ubangiji ya yi niyya, ya kuwaaikataAbin da ya faɗa a kan mazaunanBabila.
13 Ƙarshenki ya zo,Ke mai zama kusa da ruwa mai yawa,Mai yawan dukiya.Ajalinki ya auka.
14 Ubangiji Mai Runduna ya rantse dazatinsa, ya ce,“Hakika zan cika Babila da mutanekamar fāra,Za su kuwa raira waƙar nasara akanta.”