17 “Haka ni Ubangiji Mai Runduna nace,Ku yi tunani, ku kirawo mata masumakoki su zo,Ku aika wa gwanaye fa.”
18 Jama'a suka ce,“Su gaggauta, su ta da murya,Su yi mana kuka da ƙarfi,Har idanunmu su cika da hawaye,Giranmu kuma su jiƙe sharaf.
19 “Gama ana jin muryar kuka dagaSihiyona cewa,‘Ga yadda muka lalace! Aka kunyatarda mu ɗungum!Don mun bar ƙasar, domin sunrurrushe wuraren zamanmu.’ ”
20 Irmiya ya ce,“Ya ku mata, ku ji maganarUbangiji,Ku kasa kunne ga maganar da yafaɗa,Ku koya wa 'ya'yanku mata kukanmakoki,Kowacce ta koya wa maƙwabciyartawaƙar makoki,
21 Gama mutuwa ta shiga tagoginmu,Ta shiga cikin fādodinmu,Ta karkashe yara a tituna,Ta kuma karkashe samari a dandali.
22 Ubangiji ya ce mini,‘Ka yi magana, cewa gawawwakinmutane za su fāɗi tuliKamar juji a saura,Kamar dammunan da masu girbisuka ɗaura,Ba wanda zai tattara su.’ ”
23 Ubangiji ya ce, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa, kada mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa, kada kuma mawadaci ya yi fariya da wadatarsa.