4 Ba zan yi rashin aminci ba,Ba kuwa zan yi tunanin mugunta ba.
5 Zan hallakar da mai raɗar abokinsa,Ba zan jure da mutum mai girmankai,Ko mai alfarma ba.
6 Zan yarda da waɗanda suke amincewa da Allah,Zan yardar musu si yi zamansu a fādata,Zan yarda wa waɗanda suke da tabbataccen aminciSu yi mini hidima.
7 Maƙaryaci ba zai zauna a fādata ba,Ba zan yarda munafuki ya yi zamansa a wurina ba.
8 A kowace rana zan yi ta karkashe dukan mugayen da suke cikin ƙasarmu,Zan kori dukan mugaye daga birnin Ubangiji.