1 Na dogara ga Ubangiji domin zaman lafiya,Wauta ce idan kun ce mini,“Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu,
2 Domin mugaye sun ja bakkunansu,Sun kuma ɗana kibansuDomin su harbi mutanen kirki a duhu.
3 Ba abin da mutumin kirki zai iya yiSa'ad da kome ya lalace.”
4 Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa,Yana da kursiyinsa a Sama.Yana kallon dukan mutaneYana sane da abin da suke yi.
5 Yana auna masu kirki da mugaye dukka,Yana ƙin marar bin doka gaba ɗaya.
6 Yakan aukar da garwashin wutaDa kibritu mai cin wuta a kan mugaye,Yakan hukunta su da harshen wuta mai ƙuna.
7 Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar kyawawan ayyuka,Masu yi masa biyayya za su zauna a gabansa.