1 A bakin kogunan BabilaMuka zauna muka yi ta kuka,Sa'ad da muka tuna da Sihiyona.
2 A rassan itatuwan wardi da suke kusa da muMuka rataye garayunmu.
3 Waɗanda suka kama mu suka sa mu mu yi waƙa,Suka ce mana, “Ku yi mana shagaliDa waƙar da aka raira wa Sihiyona!”
4 Kaƙa za mu raira waƙar UbangijiA baƙuwar ƙasa?
5 Da ma kada in ƙara iya kaɗa garaya,Idan na manta da ke, Urushalima!
6 Da ma kada in ƙara iya raira waƙa,Idan na manta da ke,Idan ban tuna ke ceBabbar abar farin ciki ba!
7 Ka tuna, ya Ubangiji, da abin da Edomawa suka yi,A ranar da aka ci Urushalima.Ka tuna da yadda suka ce,“A ragargaza ta har ƙasa!”
8 Babila, za a hallaka ki!Mai farin ciki ne shi wanda ya sāka mikiBisa ga abin da kika yi mana.
9 Mai farin ciki ne shi wanda zai kwashi jarirankiYă fyaɗa su a kan duwatsu!