6 Ni kamar tsuntsu nake cikin hamada,Kamar mujiya a kufai.
7 Kwana nake ba barci,Na zama kamar tsuntsun da yake fama da kewaA bisa kan ɗaki.
8 Maƙiyana suna cin mutuncina dukan yini.Waɗanda suke mini ba'a,Suna la'antarwa da sunana.
9 Toka ce abincina,Hawayena kuwa sun gauraya da abin shana,
10 Sabili da fushinka da hasalarka.Ka ɗauke ni, ka jefar da ni.
11 Raina kamar inuwar maraice yake,Kamar busasshiyar ciyawa nake.
12 Amma kai, ya Ubangiji, sarki ne kai har abada,Dukan zamanai masu zuwa za su tuna da kai.