1 Ka yabi Ubangiji, ya raina!Ka yabi sunansa mai tsarki!
2 Ka yabi Ubangiji, ya raina,Kada ka manta da yawan alherinsa.
3 Ya gafarta dukan zunubaina,Ya kuma warkar da dukan cuce-cucena.
4 Ya cece ni daga kabari,Ya sa mini albarka da ƙauna da jinƙai.