10 Ubangiji ya yi madawwamin alkawari da Isra'ila,Ya yi madawwamiyar yarjejeniya da Yakubu sa'ad da ya ce,
11 “Zan ba ka ƙasar Kan'ana,Za ta zama mallakarka.”
12 Jama'ar Ubangiji kima ne,Baƙi ne kuwa a ƙasar.
13 Suka yi ta yawo daga ƙasa zuwa ƙasa,Daga wannan mulki zuwa wancan,
14 Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba,Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su.
15 Ya ce, “Kada ku taɓi bayina, zaɓaɓɓu,Kada ku cuci annabawana!”
16 Sa'ad da Ubangiji ya aukar da yunwa a ƙasarsu,Ya kuma sa abincinsu duka ya ƙare,