18 Ƙafafunsa suka yi rauni saboda an ɗaure su da sarƙa,Aka kuma sa wa wuyansa ƙuƙumi na baƙin ƙarfe,
19 Har kafin faɗar da ya yi, ta cika.Maganar Ubangiji ta tabbatar da gaskiyar abin da ya faɗa.
20 Sa'an nan Sarkin Masar ya sake shi,Mai mulkin dukan sauran al'umma ya 'yantar da shi.
21 Ya sa shi ya lura da mulkinsa,Ya sa shi ya yi mulki a bisa dukan ƙasar.
22 Ya ba shi cikakken iko bisa dukan ma'aikatan hukuma.Ya ba shi ikon umartar mashawartansa.
23 Sa'an nan Yakubu ya tafi Masar,Ya zauna a ƙasar.
24 Ubangiji ya sa jama'arsa suka hayayyafa da yawa,Ya sa su fi ƙarfin maƙiyansu.