20 Sa'an nan Sarkin Masar ya sake shi,Mai mulkin dukan sauran al'umma ya 'yantar da shi.
21 Ya sa shi ya lura da mulkinsa,Ya sa shi ya yi mulki a bisa dukan ƙasar.
22 Ya ba shi cikakken iko bisa dukan ma'aikatan hukuma.Ya ba shi ikon umartar mashawartansa.
23 Sa'an nan Yakubu ya tafi Masar,Ya zauna a ƙasar.
24 Ubangiji ya sa jama'arsa suka hayayyafa da yawa,Ya sa su fi ƙarfin maƙiyansu.
25 Ya sa Masarawa suka ƙi jinin jama'arsa,Suka yi wa bayinsa munafunci.
26 Sai ya aiki bayinsa Musa da Haruna, waɗanda ya zaɓa.