14 Ya fisshe su daga cikin duhu da inuwar mutuwa,Ya tsintsinka sarƙoƙinsu.
15 Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa,Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu.
16 Ya kakkarya ƙofofin da aka yi da tagulla.Ya kuma ragargaza ƙyamaren da aka yi da baƙin ƙarfe.
17 Waɗansu suka yi ciwo sabili da zunubansu,Suna ta shan wahala saboda muguntarsu.
18 Ba su so su ga abinci,Sun kusa mutuwa.
19 A cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji,Ya kuwa cece su daga azabar da suke sha.
20 Da umarninsa ya warkar da su,Ya cece su daga kabari.