8 Ka aukar masa da ajalinsa nan da nan,Ka sa wani ya ɗauki matsayinsa!
9 Ka sa 'ya'yansa su zama marayu,Matarsa kuwa ta zama gwauruwa!
10 Ka sa 'ya'yansa su rasa gidan zama, su riƙa yawon bara.Ka sa a kore su daga kufan da suke zaune!
11 Ka sa waɗanda suke binsa bashi su kwasheDukan abin da yake da shi.Ka sa baƙi su kwashe dukan abin da ya sha wahalar nema.
12 Ka sa kada kowa ya yi masa alheri sam,Kada ka bar kowa ya lura da marayunsa.
13 Ka sa dukan zuriyarsa su mutu,Har a manta da sunansa a tsara mai zuwa.
14 Sai ka tuna, ya Ubangiji, da muguntar kakanninsa,Kada ka manta da zunuban mahaifiyarsa.