14 Zan ba shi abin da na alkawartaA taron dukan jama'arsa.
15 Mutuwar ɗaya daga cikin tsarkakansa,Abu mai daraja ne!
16 Ni bawanka ne, ya Ubangiji,Ina bauta maka yadda mahaifiyata ta yi,Ka 'yantar da ni.
17 Zan miƙa maka hadaya ta godiya,Zan yi addu'ata a gare ka.
18-19 A taron dukan jama'arka,A shirayun Haikalinka,A Urushalima, zan ba ka abin da na alkawarta.Yabo ya tabbata ga Ubangiji!