115 Ku rabu da ni, ku masu zunubi!Zan yi biyayya da umarnan Allahna.
116 Ka ƙarfafa ni kamar yadda ka alkawarta, zan kuwa rayu,Kada ka bar ni in kasa ci wa burina!
117 Ka riƙe ni, sai in zauna lafiya,Koyaushe zan mai da hankali ga umarnanka.
118 Ka rabu da dukan waɗanda ba su biyayya da dokokinka,Dabarunsu na yaudara banza ne.
119 Kakan yi banza da duk mai mugunta,Don haka ina ƙaunar koyarwarka.
120 Saboda kai, nake jin tsoro,Na cika da tsoro saboda shari'unka.
121 Na yi abin da yake daidai mai kyau,Kada ka bar ni a hannun maƙiyana!