1 Ka cece ni, ya Ubangiji,Ba sauran mutanen kirki,Ba kuma za a sami amintattun mutane ba.
2 Dukan mutane suna yi wa juna ƙarya,Suna ruɗin junansu da yaudara.
3 Ka sa harsunan nan masu yaudara su yi shiru,Ya Ubangiji, ka rufe bakunan nan masu fāriya!
4 Sukan ce, “Za mu yi magana yadda muka ga dama,Ba kuwa wanda zai hana mu.Wane ne yake da ikon faɗa mana abin da za mu faɗa?”