1 Da zuciya ɗaya nake gode maka, ya Ubangiji,Ina raira waƙar yabonka a gaban alloli.
2 Na durƙusa a gaban tsattsarkan HaikalinkaIna yabon sunanka.Sabili da madawwamiyar ƙaunarka da amincinka,Saboda ka nuna ɗaukakarka da umarnanka.
3 Ka amsa mini sa'ad da na yi kira gare ka,Da ƙarfinka ka ƙarfafa ni.
4 Dukan sarakunan duniyar nan za su yabe ka, ya Ubangiji,Gama sun riga sun ji alkawaranka.
5 Za su raira waƙa a kan abin da Ubangiji ya yi,Za su raira waƙa kuma a kan ɗaukakarsa mai girma.