7 Kamar itacen da aka faskare, aka daddatse,Haka aka watsar da ƙasusuwansu a gefen kabari.
8 Amma ni, ya Ubangiji Allah, da nake dogara a gare ka,Ina neman kiyayewarka,Kada ka bar ni in halaka!
9 Ka kiyaye ni daga tarkunan da suka kafa mini,Daga ashiftar masu aikata mugunta.
10 Ka sa mugaye su fāɗa cikin tarkunansu,Ni kuwa in zo in wuce lafiya.