12 Ya Urushalima, ki yabi Ubangiji,Ya Sihiyona, ki yabi Allahnki.
13 Shi yake riƙe da ƙofofinki da ƙarfi,Yakan sa wa jama'arki albarka.
14 Yakan kiyaye kan iyakar ƙasarki lafiya,Yakan kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 Yakan ba da umarni,Nan da nan umarnin yakan iso duniya.
16 Yakan aiko da dusar ƙanƙara mai kauri kamar ulu,Ya watsa jaura kamar ƙura.
17 Yakan aiko da ƙanƙara kamar duwatsu,Ba wanda yake iya jurewa da sanyin da yakan aiko!
18 Sa'an nan yakan ba da umarni,Ƙanƙara kuwa ta narke,Yakan aiko da iska, ruwa kuwa yakan gudu.