3 Ka san zuciyata,Kakan zo gare ni da dare,Ka riga ka jarraba ni sarai,Ba ka kuwa sami mugun nufi a cikina ba.Na ƙudurta kuma bakina ba zai yi saɓo ba.
4 Zancen aikin sauran mutane,Na yi biyayya ga umarninkaBan bi hanyar rashin hankali ba.
5 Ina tafiya a kan tafarkinka kullum,Ban kuwa kauce ba.
6 Ina addu'a gare ka, ya Allah,Domin kakan amsa mini,Don haka ka juyo wurina ka kasa kunne ga maganata.
7 Ka bayyana ƙaunarka mai banmamaki,Ya Mai Ceto,Muddin muna kusa da kai mun tsira daga maƙiyanmu.
8 Ka kiyaye ni kamar yadda ake kiyaye idanu,Ka ɓoye ni a inuwar fikafikanka,
9 Daga hare-hare na mugaye.Maƙiyana cike da ƙiyayya sun kewaye ni.