6 Ina addu'a gare ka, ya Allah,Domin kakan amsa mini,Don haka ka juyo wurina ka kasa kunne ga maganata.
7 Ka bayyana ƙaunarka mai banmamaki,Ya Mai Ceto,Muddin muna kusa da kai mun tsira daga maƙiyanmu.
8 Ka kiyaye ni kamar yadda ake kiyaye idanu,Ka ɓoye ni a inuwar fikafikanka,
9 Daga hare-hare na mugaye.Maƙiyana cike da ƙiyayya sun kewaye ni.
10 Ba su jin tausayi, suna magana da girmankai,
11 Yanzu suna kewaye da ni duk inda na juya,Suna jira su sami dama su fyaɗa ni ƙasa.
12 Kamar zakoki suke nema su yayyage ni kaca-kaca,Kamar sagarun zakoki suna fakona a wurin ɓuyarsu.