3 Suna cewa, “Bari mu 'yantar da kanmu daga mulkinsu,Bari mu fice daga ƙarƙashinsu!”
4 Ubangiji ya yi dariya daga kan kursiyinsa can Sama,Ya mai da su abin dariya.
5 Ya yi musu magana da fushi,Ya razanar da su da hasalarsa,
6 Ya ce, “A bisa Sihiyona, dutsena tsattsarka,Na naɗa sarkina.”
7 Sarkin ya ce, “Zan yi shelar abin da Ubangiji ya hurta.Ubangiji ya ce mini, ‘Kai ɗana ne,Yau ne na zama mahaifinka.
8 Ka yi roƙo, zan kuwa ba ka dukan al'ummai,Dukan duniya kuma za ta zama taka.
9 Za ka mallake su da sandan ƙarfe,Za ka farfashe su kamar tukunyar yumɓu.’ ”