1 A gare ka nake yin addu'a, ya Ubangiji,
2 A gare ka nake dogara, ya Allah.Ka cece ni daga shan kunyar fāɗuwa,Kada ka bar magabtana su yi mini duban wulakanci!
3 Waɗanda suke dogara gare ka,Ba za su kasa yin nasara ba,Sai dai waɗanda suke gaggawa su yi maka tayarwa.
4 Ka koya mini al'amuranka, ya Ubangiji,Ka sa su zama sanannu a gare ni.