1 Dukanku adalai ku yi murna,A kan abin da Ubangiji ya yi,Ku yabe shi, ku da kuke masa biyayya!
2 Ku kaɗa garaya, kuna yi wa Ubangiji godiya.Ku raira masa waƙa, da kayan kaɗe-kaɗe masu tsarkiya.
3 Ku raira masa sabuwar waƙa,Ku kaɗa garaya da gwaninta,Ku kuma raira waƙa da ƙarfi!
4 Kalmomin Ubangiji gaskiya ne,Ayyukansa duka kuwa abin dogara ne.