10 Har zakoki sukan rasa abinci su ji yunwa,Amma masu biyayya ga Ubangiji,Ba abu mai kyau da sukan rasa.
11 Ku zo, ku abokaina, ku kasa kunne gare ni,Zan koya muku ku ji tsoron Ubangiji.
12 Kuna so ku ji daɗin rai?Kuna son tsawon rai da farin ciki?
13 To, ku yi nisa da mugun baki,Da faɗar ƙarairayi.
14 Ku rabu da mugunta, ku aikata alheri,Ku yi marmarin salama, ku yi ƙoƙarin samunta.
15 Ubangiji yana lura da adalai,Yana kasa kunne ga koke-kokensu,
16 Amma yana ƙin masu aikata mugunta,Saboda haka har mutanensu sukan manta da su.