2 Zan yabe shi saboda abin da ya yi,Da ma dukan waɗanda suke da tawali'u su kasa kunne, su yi murna!
3 Ku yi shelar girman Ubangiji tare da ni,Mu yabi sunansa tare!
4 Na yi addu'a ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini,Ya kuɓutar da ni daga dukan tsorona.
5 Waɗanda ake zalunta suka dube shi suka yi murna,Ba za su ƙara ɓacin rai ba.
6 Marasa galihu suka yi kira gare shi, ya kuwa amsa.Ya cece su daga dukan wahalarsu.
7 Mala'ikansa yana tsaron waɗanda suke tsoron Ubangiji,Ya cece su daga hatsari.
8 Ku gane da kanku yadda Ubangiji yake da alheri!Mai farin ciki ne mutumin da ya sami kwanciyar rai a wurinsa!