1 Kada ka damu saboda mugaye,Kada ka yi ƙyashin masu aikata abin da ba daidai ba.
2 Za su shuɗe kamar busasshiyar ciyawa,Za su mutu kamar yadda tsire-tsire suke bushewa.
3 Ka dogara ga Ubangiji ka aikata nagarta,Ka zauna a ƙasar, ka sami lafiya.
4 Ka nemi farin cikinka a wurin Ubangiji,Zai kuwa biya maka bukatarka.