11 Amma masu ladabi za su zauna lafiya a ƙasar,Su ji daɗin cikakkiyar salama.
12 Mugu yakan yi wa mutumin kirki makarƙashiya,Yana harararsa da ƙiyayya.
13 Ubangiji yana yi wa mugu dariya,Domin Ubangiji ya sani ba da daɗewa ba mugun zai hallaka.
14 Mugaye sun zare takuba,Sun tanƙware bakkunansuDon su kashe matalauta da masu bukata,Su karkashe mutanen kirki.
15 Amma takubansu za su sassoke su,Za a kakkarya bakkunansu.
16 Ƙanƙanen abin da mutumin kirki yake da shi,Ya fi dukan dukiyar mugaye amfani,
17 Gama Ubangiji zai raba mugaye da ƙarfinsu,Amma zai kiyaye mutanen kirki.