14 Mugaye sun zare takuba,Sun tanƙware bakkunansuDon su kashe matalauta da masu bukata,Su karkashe mutanen kirki.
15 Amma takubansu za su sassoke su,Za a kakkarya bakkunansu.
16 Ƙanƙanen abin da mutumin kirki yake da shi,Ya fi dukan dukiyar mugaye amfani,
17 Gama Ubangiji zai raba mugaye da ƙarfinsu,Amma zai kiyaye mutanen kirki.
18 Ubangiji yana kula da masu yi masa biyayya,Ƙasar kuwa za ta zama tasu har abada.
19 Ba za su sha wahala a lokacin tsanani ba,Za su sami yalwa a lokacin yunwa.
20 Amma mugaye za su mutu,Magabtan Ubangiji kuwa za su shuɗe kamar furen jeji,Za su ɓace kamar hayaƙi.