36 Amma bayan ƙanƙanen lokaci,Da na zaga, ban gan shi ba,Na neme shi, amma ban same shi ba.
37 Dubi mutumin kirki, ka lura da adali,Mutumin salama yakan sami zuriya,
38 Amma za a hallaka masu zunubi ƙaƙaf,Za a kuma shafe zuriyarsu.
39 Ubangiji yakan ceci adalai,Ya kiyaye su a lokatan wahala.
40 Yakan taimake su, yă kuɓutar da su,Yakan cece su daga mugaye,Gama sukan zo wurinsa don yă kāre su.