37 Dubi mutumin kirki, ka lura da adali,Mutumin salama yakan sami zuriya,
38 Amma za a hallaka masu zunubi ƙaƙaf,Za a kuma shafe zuriyarsu.
39 Ubangiji yakan ceci adalai,Ya kiyaye su a lokatan wahala.
40 Yakan taimake su, yă kuɓutar da su,Yakan cece su daga mugaye,Gama sukan zo wurinsa don yă kāre su.