9 Waɗanda suka dogara ga Ubangiji,Za su yi zamansu lafiya a ƙasar,Amma za a kori mugaye.
10 A ɗan ƙanƙanen lokaci mugaye za su shuɗe,Za ka neme su, amma ba za a same su ba,
11 Amma masu ladabi za su zauna lafiya a ƙasar,Su ji daɗin cikakkiyar salama.
12 Mugu yakan yi wa mutumin kirki makarƙashiya,Yana harararsa da ƙiyayya.
13 Ubangiji yana yi wa mugu dariya,Domin Ubangiji ya sani ba da daɗewa ba mugun zai hallaka.
14 Mugaye sun zare takuba,Sun tanƙware bakkunansuDon su kashe matalauta da masu bukata,Su karkashe mutanen kirki.
15 Amma takubansu za su sassoke su,Za a kakkarya bakkunansu.