5 Ku miƙa wa Ubangiji hadayun da suka dace,Ku kuma dogara gare shi.
6 Akwai mutane da yawa da suke cewa,“Da ma a sa mana albarka!”Ka dube mu da alheri, ya Ubangiji!
7 Farin cikin da ka ba ni mai yawa ne,Fiye da na waɗanda suke da wadataccen hatsi da ruwan inabi.
8 Da zarar na kwanta, sai barci ya kwashe ni,Kai kaɗai kake kiyaye ni sosai, ya Ubangiji.