10 Ka sa muka gudu daga gaban abokan gābanmu,Suka ƙwace abin da muke da shi.
11 Ka bari aka yanyanka mu kamar tumaki,Ka warwatsar da mu a baƙuwar ƙasa.
12 Ka sayar da jama'arkaA bakin 'yan kuɗi ƙalilan,Ba ka ci ribar cinikin ba.
13 Maƙwabtanmu suna yi mana dariya saboda kai,Suna yi mana ba'a, sun maishe mu abin wasa.
14 Ka maishe mu abin raini a wurin arna,Suna kaɗa mana kai, suna raina mu.
15 Kullum a cikin kunya nake,Kunya ta lulluɓe ni ɗungum,
16 Saboda dukan wulakanci,Da zagin da nake sha daga maƙiyana da abokan gābana.