7 Amma ka cece mu daga abokan gābanmu,Ka kori waɗanda suke ƙinmu.
8 Za mu yabe ka kullum,Mu yi maka godiya har abada.”
9 Amma yanzu, ya Allah, ka yashe mu,Ka bari aka kore mu,Ba ka ƙara fita ka yi tafiya tare da sojojinmu ba.
10 Ka sa muka gudu daga gaban abokan gābanmu,Suka ƙwace abin da muke da shi.
11 Ka bari aka yanyanka mu kamar tumaki,Ka warwatsar da mu a baƙuwar ƙasa.
12 Ka sayar da jama'arkaA bakin 'yan kuɗi ƙalilan,Ba ka ci ribar cinikin ba.
13 Maƙwabtanmu suna yi mana dariya saboda kai,Suna yi mana ba'a, sun maishe mu abin wasa.