10 Ki ji abin da zan faɗa, ya ke amaryar sarki,Ki manta da mutanenki da danginki.
11 Saboda ke kyakkyawa ce sarki zai so ki,Shi ne maigidanki, sai ki yi masa biyayya.
12 Mutanen Taya za su kawo miki kyautai,Attajirai za su zo su sami farin jini a gare ki.
13 Gimbiya tana fāda, kyakkyawa ce ainun,Da zaren zinariya aka saƙa rigarta,
14 Aka kai ta wurin sarki tana saye da riga mai ado.Ga 'yan matanta a biye,Aka kawo su wurin sarki.
15 Da farin ciki da murna suka zo,Suka shiga fādar sarki.
16 Za ka haifi 'ya'ya maza da yawa,Waɗanda za su maye matsayin kakanninka,Za ka sa su zama masu mulkin duniya duka.