5 Kibanka suna da tsini,Suna huda zuciyar abokan gābanka,Al'ummai suna fāɗuwa ƙasa a ƙafafunka.
6 Kursiyinka, ya Allah, zai dawwama har abada abadin!Kana mulkin mallakarka da adalci.
7 Kana ƙaunar abin da yake daidai,Kana ƙin abin da yake mugu.Saboda haka Allah, Allahnka, ya zaɓe ka,Ya kuwa kwararo maka farin ciki mai yawa fiye da kowa.
8 Tufafinka suna ƙanshin turaren mur, da na aloyes, da na kashiya,A kowace fādar hauren giwa, mawaƙa suna yi maka waƙar.
9 Daga cikin matan da suke fadarka, har da 'ya'yan sarakuna.A daman kursiyinka kuwa ga sarauniya a tsaye.Tana saye da kayan ado na zinariya mafi kyau duka.
10 Ki ji abin da zan faɗa, ya ke amaryar sarki,Ki manta da mutanenki da danginki.
11 Saboda ke kyakkyawa ce sarki zai so ki,Shi ne maigidanki, sai ki yi masa biyayya.