10 Ka halitta tsarkakakkiyar zuciya a cikina, ya Allah,Ka sa sabon halin biyayya a cikina.
11 Kada ka kore ni daga gabanka,Kada ka ɗauke mini Ruhunka Mai Tsarki.
12 Ka sāke mayar mini da farin ciki na cetonka,Ka ƙarfafa ni da zuciya ta biyayya.
13 Sa'an nan zan koya wa masu zunubi umarnanka,Za su kuwa komo wurinka.
14 Ka rayar da raina, ya Allah Mai Cetona,Zan kuwa yi shelar adalcinka da farin ciki.
15 Ka taimake ni in yi magana, ya Ubangiji,Zan kuwa yabe ka.
16 Ba ka son sadakoki, ai, da na ba ka,Ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.