5 Maƙiyana suke ta wahalshe ni dukan yini,A kan kowane abu da nake yi,Kullum suna ta tunanin yadda za su cuce ni!
6 Sukan taru a ɓoye,Suna kallon duk abin da nake yi.Suna sa zuciya za su iya kashe ni.
7 Ka hukunta su, ya Allah saboda muguntarsu,Da fushinka ka kori waɗannan mutane!
8 Ka san irin wahalar da nake sha,Kana riƙe da lissafin yawan hawayena.Ashe, ba a rubuce suke a littafinka ba?
9 A ranar da na yi kira gare ka,Za a komar da abokan gābana baya,Gama na sani Allah yana tare da ni!
10 Ina dogara ga Allah, ina yabon alkawarinsa,Ina dogara ga Ubangiji, ina yabon alkawarinsa.
11 A gare shi nake dogara,Ba zan ji tsoro ba.Me mutum kawai zai yi mini?