1 Ya Ubangiji, kada ka yi fushi, ka kuma tsauta mini!Kada ka hukunta ni da fushinka!
2 Ka ji tausayina, gama na gaji tiƙis,Ka wartsarkar da ni, gama na tafke sarai.
3 Duk na damu ƙwarai da gaske.Sai yaushe wannan zai ƙare, ya Ubangiji?
4 Ya Ubangiji, ka zo ka cece ni,Gama kana ƙaunata, ka kuɓutar da ni daga mutuwa.
5 Ba za a tuna da kai a lahira ba,Ba wanda zai yabe ka a can!