6 A duk kwanakina a gare ka nake dogara,Kana kiyaye ni tun da aka haife ni,Kullayaumi zan yabe ka!
7 Raina abin damuwa ne ga mutane da yawa,Amma kai ne kāriyata mai ƙarfi.
8 Ina yabonka dukan yini,Ina shelar darajarka.
9 Yanzu da na tsufa, kada ka yashe ni,Yanzu da ƙarfina ya ƙare kuma, kada ka rabu da ni!
10 Maƙiyana, waɗanda suke so su kashe ni,Suna magana, suna ƙulle-ƙulle gāba da ni.
11 Suna cewa, “Ai, Allah ya rabu da shi,Gama ba wanda zai cece shi!”
12 Kada ka yi nisa da ni haka, ya Allah,Ka yi hanzari ka taimake ni, ya Allahna!