5 “Waɗanne irin jahilai ne ku, wawaye!Kuna zaune cikin duhu,Ga shi, ba adalci a duniya sam!
6 Na faɗa muku, ku alloli ne,Cewa dukanku 'ya'ya ne na Maɗaukaki.
7 Amma za ku mutu kamar kowane mutum,Ku fāɗi kamar kowane basarauce.”
8 Ya Allah, ka zo, ka mallaki duniya,Dukan al'ummai naka ne.