21 Ƙarfina zai kasance tare da shi,Ikona kuma zai ƙarfafa shi.
22 Abokan gābansa ba za su taɓa cin nasara a kansa ba,Mugaye ba za su kore shi ba.
23 Zan ragargaza magabtansa,In karkashe duk waɗanda suke ƙinsa.
24 Zan ƙaunace shi kullum, in amince da shi,Zan sa ya yi nasara kullayaumin.
25 Zan faɗaɗa mulkinsa tun daga Bahar Rum,Har zuwa Kogin Yufiretis.
26 Zai ce mini, ‘Kai ubana ne da Allahna,Kai ne kake kiyaye ni, kai ne Mai Cetona.’
27 Zan maishe shi ɗan farina,Mafi girma daga cikin dukan sarakuna.