17 Mutuwa ce maƙarar dukan mugaye,Da dukan waɗanda suke ƙin Allah.
18 Ba kullum ne ake ƙyale masu bukata ba,Ba za a danne sa zuciyar waɗanda ake zalunta ba har abada.
19 Ka zo, ya Ubangiji! Kada ka bari mutane su gagare ka!Ka kawo arna a gabanka, ka hukunta su.
20 Ka sa su ji tsoro, ya Ubangiji,Ka sa su sani su mutane ne kawai.