5 Ka kā da arna,Ka kuma hallakar da mugaye,Ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba.
6 An hallaka abokan gābanmu har abada,Ka lalatar da biranensu,An kuma manta da su sarai.
7 Amma Ubangiji sarki ne har abada,Ya kafa kursiyinsa domin yin shari'a.
8 Yana mulkin duniya da adalci,Yana yi wa mutane shari'a da gaskiya.
9 Ubangiji mafaka ne ga waɗanda ake zalunta,Wurin ɓuya a lokatan wahala.
10 Waɗanda suka san ka za su amince da kai, ya Ubangiji,Ba za ka ƙyale duk wanda ya zo gare ka ba.
11 Ku yabi Ubangiji, shi da yake mulki a Sihiyona!Ku faɗa wa kowace al'umma abin da ya yi!